Wednesday 11 October 2017

ARBAUNA HADITH SHEIK JAAFAR MAHMUD ADAM Ana kiranshi da suna Al-Arba'unan

ARBAUNA HADITH
SHEIK JAAFAR MAHMUD ADAM
Ana kiranshi da suna Al-Arba'unan nawawiyya saboda jinginashi ga malami Al-imamu yahaya bn shafi'i annawawi shine marubucin littafin haka nan ana iya kiranshi da suna har guda uku:Annawawi,Annawawiy,Annawa'i.jinginawa ce zuwa ga mahaifar sa

DOWNLOAD AUDIOS
COMPLETE HADITH HERE

Contact us 08131240056

COMPLETE AL-QUR'AN (AS-SUDIES)

Quran Recitation by As-Sudais
Bismillah ir-Rahman ir-Rahim.
The FreeQuranMP3.com crew humbly seeks the pleasure of Allah Subhanahu Wa Ta'ala by providing you with the complete Quran recitation by Sheikh Abdur-Rahman As-Sudais.
Download, listen and share with others, insha'Allah.
Quran Mp3 files
Sheikh Abdur-Rahman As-Sudais' FULL/COMPLETE Quran recitation, in a zipped folder consisting of 114 surah mp3 files, can be downloaded HERE (1.2GB).



DOWNLOAD ALL HERE
COMPLETE QUR'AN

Contact us
08131240056

Tuesday 3 October 2017

TAUHIDI (kadaita Allah)

TAUHIDI (kadaita Allah)


Dasunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai
TAUHIDI (kad'aita Allah)
Shine kadaita Allah a cikin Bauta shi kadai batare da hadashi da wani ba, kuma shine Addinin da aka aiko Annabawa dashi gaba dayaAllah yakara masu Aminci, kuma Allah baze karbi wani Addini ba inba shiba, kuma baya karban Ayyukan bayi se dashi, domin shine Asalin da ake gina Addini akanshi, kuma duk sanda aka rasashi to aikin bawa baze amfane shiba. KARKASUWAN TAUHIDI Tauhidi yakasu zuwa kashi uku (3):
1. Tauhidin Rububiyyah (Reno) Shine kudurce cewa Allah, shine wanda ya halicci, dukkan halittu, yake azurtasu, kuma wannan Nau’i na Tauhidi babu wanda yake musunshi, har mushrikan farko sun tabbatar dashi, kamar su Abu Jahal, fir’auma ne kawai wanda yatabayin musun babu ubangiji, sun kasance suna shedawa cewa Allah shine wanda yake halitta, yake gudanar dakomai dake cikin duniya, shike rayawa, yake kashewa, Allah madaukakin Sarki yace “Kuma idan kuka tambayesu wanene wanda yahalicci Sammai da Kassai, yake gudanar da Rana da Wata? Tabbas zasuce maka shine Allah…..( Sur.Ankabut: 61) Se ikirarin dasu kayi be shigar dasu musulunci ba, kuma baze tseratar dasu daga Azaba ba, kuma bata kare masu dukiyoyinsu da dukiyoyinsu ba, saboda basu tabbatar da Tauhidin Uluhiyyah, sun hada Allah da wani cikin bauta.
2. Tauhidin Uluuhiyyah (Bauta) Shine kadaita Allah acikin dukkan Ayyukan bauta da ake kusanci zuwa ga Allah dasu, kamar Addu’a da Tsoro,da Fata, da Dogaro, da Kwadayi, da Tsorata, da Neman temako, da neman biyan bukaya, da yin yanka da Alwashi da makamantansu. Kuma Allah yasaukarwa manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam (“Kace an umarceni ne da in bautawa Allah ina me kadaita masa Addini” Sur. Zumar 11.) wato bauta Saboda haka mutum baze juya wani daga cikin ibada bag a wani daya daga cikin mala’iku ko wani Annabi ko wani Waliyyi ko Shehi, domin hakki ne na Allah, wanda kon yaba wanda bashi ba to yayi Shirka.
3. Tauhidin Asmaa’u was Siffat Shine imani da cewa Allah yana da zati wanda baya kama da sauran zatuttuka, yana da siffofin da b asa kamada sauran siffofi, kuma sunayensa suna nuni ne nuni na yanke shakka akan abinda abinda yake dashi na siffofin cika wayo kamala kai tsaye. Allah Subhanahu Wata’ala yace (“Babu wani abu da yayi kama dashi kuma shi me jine me gani “ Sur. Shuurah 11.) kuma da tabbatar da abinda Allah ya tabbatar ma kansa acikin littafinsa (Al’qur’ani)ko manzansa yatabbatar masa dashi tabbatarwa wacce take dacewa da girma da daukakarsa ba tare da kamantashi da wani abu ba, ko kwatantashi da wani ba, ko kore masa sifar, ko lankwasa ma’anarsa, ko yanda yake, baza muyi kokarin kamanta wani sashi na cikin siffofinsa ba da zukatanmu ko da tunaninmu, A’ah zmu bar abin kamar yanda yabamu labari. TO YAYA ZAMU SAMU TAUHIDI?
Zamu iya zama masu tauhidi ne, ta hanyar sanin Allah, wanene shi? da sanin hakikaninsa, a ilmance da kuma aiki da hakan, kuma shine Rai tajawu ko zuciya zuwa gareshi da soyaiya, da tsoro, da komawa zuwa gareshi, da dogaro akanshi, da Addu’a, da tsarkakeshi, da girmamashi da kuma yimasa bauta. Atakaice dai kada yazamana a zuciyar dan Adam daba na Allah ba, kuma bawa yazama baya nufin Allah da Shirka ko Bid’ah ko Sabo karaminsa da babbansa,kuma kada ya nuina kiyaiya ga duk abinda Allah yayi Umarni dashi to wannan tauhidi da kansa wato Laa ilaa ha illal Lah. MENENE MA’ANAR LAA’ILAA’HA ILLAL LAHU?
Ma’ana shine babu abin da’ake bautawa da cancanta a Sama da Kasa face Allah shi kadai baya da abokin taraiya, domin abubuwan da’ake bauta mawa baatattu suna da yawa, se dai abinda ya can-can ci bautan shine Allah shi kadai.Allah Subhanahu Wata’ala yace: (“ Saboda haka Allah shine Ubangiji na gaskiya, kuma tabbas an\binda suke kira wanda bashi baataccene, kuma lallai Allah shine madaukaki kuma me girma” Sur.alhajj:62) ba ma’anarta ba Babu mahalicci se Allah kamar yadda wadansu jahilai suke tsammani, domin kafiran Kuraishawa wanda Allah ya’aikoda manzo a cikinsu sun kasance suna sheda cewa Allah shine mahalicci me gudanar da al’amuran duniya shi kadai baya da abokin taraiya kamar yanda Allah yace: (“Shin yanzu za’a sanya Abin bauta yazama ubangiji guda daya Lallai wannan abune me ban mamaki” Sur. Saad:5) sun fahimci cewa wannan kalma lallai tana bata bautawa duk wanda ba Allah ba, kuma tana takaita bauta ga Allah shi kadai sukuma basa son haka, saboda hakane manzan Allah ya yakesu har se sun Shaida da Laa ilaa ha illal laahu kum subata hakkinta, shine kadaita Allah da bauta shi kadai. Wanna ke bata ikirarin da wadansu keyi cewa ma’anar Laa ila ha illal laahu shine kace Allah yana nan kuma shine wanda yayi halitta, yake gudanar da al’amura kuma wanda yayi hakan yana da Tauhidi koda yayi ma wani bauta kamar Rokon wadanda suka mutu suke cikin kabari,d yimusu alwashi, da neman kusancinAllah tahanyarsu, da neman Albarka (tabarruki) da yin dawafi a kabarbura da neman albarka da kasar kabarin kamar yanda muke ganin a kabarin Shehu dan fodio dake sokoto. Hakika kafiran Kuraishawa sun san cewa Laa ilaa ha illal lahu tana bukatan aiki shine barin bautawa wanda ba Allah ba, kuma idan suka fadeta suka cigaba da bauta ma gumaka to zasu war-ware musuluncinsu sukuma bas son haka sukeba, abin mamaki yau zaka musulmi suna bauta ma Allah kuma suna neman temakon wanda ba Allah, suna kiran sunayen wasu matattu na mutanen kwarai, suna war-ware musuluncinsu. Tur da wanda Abu jahal, da Abu lahab suka fisu sanin ma’anar laa ilaa ha illal lahu.
RUKUNNAN KALMAR TAUHIDI
Kalmar tauhidi tana da rukunnai guda biyu (2). korewa: tana kore bautan kowani irin abin bauta. Tabbatarwa: tana tabbatar da bauta ga Allah madaukakin Sarki shi kadai batareda hadashi da wani ba. MENENE KE WAR-WARE KALMAR TAUHIDI?
Abubuwan dasuke war-ware (bata) Kalmar tauhidi suna da yawa, amma ga wadansu daga ciki:
Na Farko: Shirka da Allah a cikin bauta , Allah madaukakin Sarki yace: (“Lallai Allah baya gafartama wanda yahada shi dawani, amma yana gafarta ma abinda ba haka ba (shirka) ga wanda yaso” Sur.Nisaa’i:116) kuma yace: (“lalai ne duk wanda yayi Shirka da Allah, to hakika Allah ya haramta masa Aljanna, kuma makomansa itace wuta, kuma Azzalumai basu da wani me temako” Sur.ma’idah:72) kuma yana daga cikin shirka, kiran wani da ba Allah ba, Idan wata musiba (fitina) tazo, yi ma Aljanu yanka ko kabari.
Na Biyu: Duk wanda yasanya wani tsakaninsa da Allah, yana Rokonsu, yana kiransu, yana neman cetonsu, yana dogaro a kansu, ya kafirta da ijmaa’in malaman musulunci.
Na Uku: Duk wanda be kafirta mushrikai ba ko yayi shakkan kafircinsu, ko yake gyara abinda suke akai kaman yan gurguzu. To ya kafirta.
Na Hudu: Duk wanda yake kudurin cewa shiryawan da ba ta Annabi ba, shi yafi cika da dai-dai akan shiryarwar manzan Allah Sallal lahu alaihi wasallam, ko hukuncin wani yafi hukuncinsa, kamar wanda yake fifita tsarin turawa akan Shri’ar musulunci to ya kafirta.
Na Biyar: Duk wanda ya kyamaci wani daga cikin abinda manzan Allah yazo dashi to koda yayi aiki dashi ya kafirta Allah madaukakin Sarki yace (“Hakan saboda kafirai sun kyamaci abinda Allah ya saukar se yabata ayyukansu”Sur.muhammad:9) Na Shida: Duk wanda yayi izgili da wani abu dake cikin Addinin da manzon Allah yazo dashi, ladan dake ciki, ko azaban dake ciki ya kafirta Allah madaukakin Sarki yace (“kace masu shin yanzu da Allah, da Ayoyinsa, da manzansa kuke yiwa izgili? Kada kukawo uzuri hakika kunzama kafirai bayan kuna masu imani...Sur.tauba:65-66)
Na bakwai: Sihiri duk wanda ya aikatashi ko ya yardaq dashi,ya kafirta Allah madaukakin Sarki yace: (“ kuma basa karantar da kowa sihiri – aljanu – face .........................................................................................
Na takwas: duk wanda.............. zamu cigaba isha Allah

Contact us 08131240056

YANDA AKE WANKAN JANABA DAGA MARIGAYI SHEK JAFAR

YADDA AKE WANKAN JANABA, HAILA, BIKI DA DAI SAURAN SU.Daga Marigayi Sheikh Jafar Mahmud Adam Kano.Wankan Janaba yana da siffa guda biyu: Akwai 'siffatul ijza' (ta wadatar), kuma wacce ake kira 'siffatu kamal' (ta kamala).Wankan Janaba a siffar sa ta kamala shi ne: Idan kazo zaka yi ko za kiyi wanka ga ruwa a gabanka. Farkon abin da zaka fara yi shi ne:zaka karkato bakin mazubin ruwanka, ka wanke hannunka sau uku, sannan sai ka tsoma hannu a cikin ruwan sai ka debo ka wanke gaban ka، a dai-dai lokacin da zaka wanke gaban ka a lokacin zaka kulla niyya ta wankan janaba (Ko waninsa) wanda yake wajibi ne, idan ka wanke gabanka ma'ana kayi tsarki kenan، to daga nan kuma sai kayialwala irin yanda kake alwala ta sallah, abin da duk kake a alwala ta sallah zakayi sai abu daya shi ne wanke kafafu to wannan zaka kyale shi ba zaka yi shiba, to daga nan sai ka tsoma hannunka guda biyua cikin ruwan ba tare da ka debo ruwa ba sai ka murmurza kanka saboda kowane gashi da ya bude a lokacin da maniyyi yake kokarin fita daga jikinka ya koma yanda yake, don gashin dan Adam yakan bude musammam gashin sa na ka, idan ka zuba ruwa a haka na iya haifar maka da ciwon kai ko wani abu daban, bayan haka sai ka debi ruwa a cikintafin hannun ka daya sai ka zuba a kanka ka tabbatar ya game ko'ina a kanka, ka sake kanfata na biyu ka tabbatar ya game ko'ina a kanka, haka nauku ka tabbatar ya game ko'ina a kanka.To idan kayi wannan sai ka debi ruwa ka game dukkanin jikin ka da shi kana mai farawa da bangaren jikin ka na dama kafin na hagu, sannan nahagu ka tabbatar ruwa ya taba ko'ina. To idan kayi wannan ne ka kammala, abu na karshe shi ne sai kawanke kafar ka ta dama sannan kafarka ta hagu shine cikon alwalar da ka riga ka faro. Wannan ita ce siffa ta kamala a wankan janaba.In wankan janaba ne haka zakayi, in na haila ne haka za'ayi inma wanka ne na biki haka mace zata yi, idan wankan jumu'a ne ma haka za'ayi, wankan idi ma haka zaka yi, banbanci kawai shi ne NIYYA.Idan mutum zai yi siffa ta 'Al ijza' wadda ta wadatar ba sai kayi alawa acikin ta ba, kana zuwa kayi niyyaryin wanka din kawai sai ka dauki ruwan ka watsa a jikin ka ya game ko'ina, inma wani kududdufi ne ko rami ko swimming pool sai kayi tsalle ka fada aciki, dama ka kulla niyyar ka kafin ka shiga, daga ka fito abin da zakayi shi ne abubuwa guda biyu, kurkurar baki da kuma shaka ruwa a hanci da facewa.Shike nan, kuma ya halatta kayi sallah da wannan wankan, Hadisi cikin Sahihu Muslim ya nuna haka.Sai dai wanda ya yi wanka na farko ya fika kamala saboda ya bi dukkan sharuddan, ya fika cikar kamala, ya fika lada.Kasancewar ba'ayi alwala ba ciki, wannan ka'idace ta malamai cewa karamin kari (HADATHUL ASGAR)idan sun hadu da babban kari (HADATHUL AKBAR) to da ka kawar da babban kari, karamin ma ya tafi. Amma ba lallai bane idan ka kawar da karamin ace babban ma ya tafi.Bissalam

YANDA AKE GABATARDA SALLAR GAWA

Yanda Ake gabatar da sallar gawa

Yanda Akeyin Sallar gawa daga Annabi (saw).Kamar yanda wasu daga cikin 'yan uwa  Suka nema cewa Ayiwa mutane Karin bayani Akan Sallar Jana'iza Muna Rokon Allah ya bamu dacewa cikin Abunda zamu fada.Da farko dai mutum Zai Qudurta Niyya a ransa.Idan Namiji ne mamacin Sai liman ya tsaya saitin kan sa, Idan Mace ce Sailiman ya tsaya tsakiyar ta daidai.Sai yayi kabbara ta farko, sai Fathi daya da sura cikin gajerunSurori ko wasu Ayoyia takaice Sai ya sake Kabbara ta biyu, sai ya kawo Salati ga Annabi (saw) Salatu Ibrahimiyya. Sai yayikabbara ta Uku, bayan kabbara ta Uku sai ya kawo wannan Adu'ar(ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻏﻔﺮ ﻟﺤﻴﻨﺎ ﻭﻣﻴﺘﻨﺎ ﻭﺷﺎﻫﺪﻧﺎ ﻭﻏﺎﺋﺒﻨﺎ ﻭﺻﻐﻴﺮﻧﺎ ﻭﻛﺒﻴﺮﻧﺎ ﻭﺫﻛﺮﻧﺎ ﻭﺃﻧﺜﺎﻧﺎ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻣﻦ ﺃﺣﻴﻴﺘﻪ ﻣﻨﺎ ﻓﺄﺣﻴﻪ ﻋﻠﻰ ﺍﻹﺳﻼﻡ، ﻭﻣﻦ ﺗﻮﻓﻴﺘﻪ ﻣﻨﺎ ﻓﺘﻮﻓﻪ ﻋﻠﻰ ﺍﻹﻳﻤﺎﻥ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻏﻔﺮ ﻟﻪ ﻭﺍﺭﺣﻤﻪ ﻭﻋﺎﻓﻪ ﻭﺍﻋﻒ ﻋﻨﻪ،ﻭﺃﻛﺮﻡ ﻧﺰﻟﻪ ﻭﻭﺳﻊ ﻣﺪﺧﻠﻪ، ﻭﺍﻏﺴﻠﻪ ﺑﺎﻟﻤﺎﺀ ﻭﺍﻟﺜﻠﺞ ﻭﺍﻟﺒﺮﺩ، ﻭﻧﻘﻪ ﻣﻦ ﺍﻟﺨﻄﺎﻳﺎ ﻛﻤﺎ ﻳﻨﻘﻰ ﺍﻟﺜﻮﺏ ﺍﻷﺑﻴﺾ ﻣﻦ ﺍﻟﺪﻧﺲ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺃﺑﺪﻟﻪ ﺩﺍﺭﺍًﺧﻴﺮﺍً ﻣﻦ ﺩﺍﺭﻩ، ﻭﺃﻫﻼ ﺧﻴﺮﺍً ﻣﻦ ﺃﻫﻠﻪ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺃﺩﺧﻠﻪ ﺍﻟﺠﻨﺔ ﻭﺃﻋﺬﻩ ﻣﻦ ﻋﺬﺍﺏ ﺍﻟﻘﺒﺮ ﻭﻣﻦ ﻋﺬﺍﺏﺍﻟﻨﺎﺭ، ﻭﺍﻓﺴﺢ ﻟﻪ ﻓﻲ ﻗﺒﺮﻩ ﻭﻧﻮﺭ ﻟﻪ ﻓﻴﻪ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻻﺗﺤﺮﻣﻨﺎ ﺃﺟﺮﻩ ﻭﻻ ﺗﻀﻠﻨﺎ ﺑﻌﺪﻩ)Idan macece sai ya canza lamirin Hi Hi Hi Hi Hi Zuwa Ha HaHa Ha Ha. Sai yayi kabbara ta Hudu, bayan kabbara ta Hudu Sai ya dan saurara Kadan sai yayi Sallama daya Gefen damar sa.Ya Allah kasa mucika da Imani Dan Alfarmar AnnabiMuhammadu (saw)
Daga Musa Muhammad Muktar burniwa
08131240056
Zaka Iya kiranmu domain wani kuskure dakaga muyi ko badadaiba
Kokuma bamu wani Abu dakaga ya dace muyi postin nasa

ARBAUNA HADITH SHEIK JAAFAR MAHMUD ADAM Ana kiranshi da suna Al-Arba'unan

ARBAUNA HADITH SHEIK JAAFAR MAHMUD ADAM Ana kiranshi da suna Al-Arba'unan nawawiyya saboda jinginashi ga malami Al-imamu yahaya bn sh...